[ad_1]
Ministan Shari’a, Abubakar Malami ya tabbatar da cewa Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki bai da alaka da harin da aka kai a wasu bankuna a garin Offa da ke jihar Kwara inda aka kashe mutane 31.
Ministan Shari’ar ya nuna cewa rundunar ‘yan sandan ba ta da kwararan shaidu da ke nuna cewa Saraki da kuma Gwamnan Kwara suna da hannu kai tsaye wajen daukar nauyin Fashi da makamin bankuna.
[ad_2]