
Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araqchi, ya isa birnin Najaf na ƙasar Iraƙi domin halartar bikin Arbaeen, kamar yadda hukumomin Iran suka tabbatar.
Araqchi ya wallafa hotonsa bayan saukarsa a Najaf ta shafinsa na Telegram.
Ziyarar tasa na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce za a fara tattaunawa tsakanin Amurka da Iran a ranar Litinin. Sai dai kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran, Esmail Baghaei, ya ce ba su da wani bayani kan sanarwar da Trump ya yi game da tattaunawar.