Me ya sa matan Arewa suke auren ‘yan kudu a yanzu?

‘Yan matan Arewa da yawa na auren samarin kudancin Najeriya – wani abu wanda ya zama salo a halin yanzu da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin kasar.

Sama da shekara 100 tun bayan da turawan mulkin mallaka na Birtaniya suka hada Arewa da kudancin najeriya, ba a taba samun wani lokaci da ake samun auratayya tsakanin kabilun najeriya ba kamar yanzu.

Mun samu zantawa da Hadiza Usman Yaro da Maryam Ladan, wasu mata biyu na Arewa dake auren ‘yan kudu domin mu ji daga gare su.

Yadda su ka hadu da mazajen nasu

“Mun hadu a wajen bikin kawata ne inda aka gaya mini cewa yana so na. Na ce me zai hada Hadiza da Mobolagi” a cewar Hadiza yaro.

Hadiza ta bayyana mana cewa bata bashi wani muhimmanci ba saboda ta san yadda sha’anin auren wani kabila yake a kudu.

Hadiza ta bayyana soyayya da shaukin juna ya kama su inda har ya kai su ga aure da samun zuriya a halin yanzu.

Ita Maryam a bangare daya, ta bayyana cewa sun hadu a jami’a ne a Malaysia. Ta nemi taimako ne daga wajensa inda daga baya soyayyay ta mamaye zuciyoyinsu.


Amarya Maraym Banufiya ce shi kuma angonta Sahed Bayarabe ne
.

“Tun bayan da muka hadu sai nace wa kaina, ke wannan Bayarabe ne, me zai hada ki da shi?” a cewar Maryam.

Kalubalen da suka fuskanta kafin aure

A cewar Maryam, bayan da ta kammala karatunta ta dawo gida Najeriya, ta fada masu ga abin da ake ciki “amma mahafina yace kwata-kwata bai yadda ba.”


Soyayya ruwan zuma in ka sha ka ba masoyi

“Yan’uwana da mahaifiyata duka suna goyon baya na, mahaifina ne kawai bai yadda ba daga farko” a cewar ta.


Soyayya gaman jini ce: Ango da Amaryasa

Maryam ta bayyana cewa hakan kwata-kwata bai gigiza Sahed ba. Har ma yake ce mata ta yi wa iyayenta biyayya, idan Allah ya kaddara aurensu, to za a yi.

Shi ma Mahaifinsa bai yadda ba daga fari, amma mahaifiyarsa na goyon bayan abin a cewar Maryam.

Daga baya Allah ya yi ikonsa gashi yanzu suna matsayin mata da miji.

Hadiza Yaro kamar Maryam, da ta bayyana soyayyarta sai mahaifiyarta ta shawarce ta da ta bar zancen don ba wani abu bane mai yiyuwa.

Amma ita ta samu goyon bayan mahaifinta. “Mahaifina yace tun da ba ita tace tana so ba ai shikenan. Idan an auramata ai ita za ta zauna da shi”

Shin mazan kudu Yarabawa sun fi na Arewa Hausa iya rikon mata?

A cewar Hadiza, ‘yan kudu idan suka sami ‘yar Arewa, “Yadda suke tarairayarmu abin kamar ba a duniyan nan ba. Ji suke kamar su yi wata nasara babba”

Hadiza ta bayyana cewa rashin yin kishiya na daga cikin abubuwan da ya sanya yanzu ‘yan matan Arewa suke auren ‘yan kudu.

A cewar Maryam, “Wannan maganan na cewa sun iya rike mata haka yake.”

Ta yi karin bayani cewa yadda ake taso da ‘yan Arewa ya sha banban dana kudu. Domin a can ana koya masu kula da gida sabanin nan Arewa da idan namiji na taimakawa a gida sai a ringa yi masa wani irin kallo.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...