Mayakan Boko Haram sun harbe sojoji 6

Rahotanni na nuni da cewa mayakan Boko Haram sun kashe a kalla sojoji shida a wani hari kan sansanin sojoji dake kauyen Kareto a karamar hukumar Mobbar ta jihar Borno.

Yan ta’addar dake kan babura sun farma sansanin sojan da misalin karfe 7 na daren ranar Alhamis.

Harin na ranar Alhamis na zuwa ne kasa da wata guda bayan da mayakan suka kashe jami’an soja sama da 25 lokacin da suke tsaka da sauyawa mutanen wani kauye matsuguni.

Wata majiya ta fadawa jaridar The Cable cewa mayakan na Boko Haram sun shafe sama da sa’o’i uku suna musayar wuta da sojojin a harin na ranar Alhamis.

A cikin wadanda aka kashe a farmakin akwai kwamandan bataliya ta 158 ya yin da wasu daga cikin sojojin ba a san halin da suke ciki ba har ya zuwa lokacin da jaridar ke hada wannan rahoto.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...