Mayakan Boko Haram sun harbe sojoji 6

Rahotanni na nuni da cewa mayakan Boko Haram sun kashe a kalla sojoji shida a wani hari kan sansanin sojoji dake kauyen Kareto a karamar hukumar Mobbar ta jihar Borno.

Yan ta’addar dake kan babura sun farma sansanin sojan da misalin karfe 7 na daren ranar Alhamis.

Harin na ranar Alhamis na zuwa ne kasa da wata guda bayan da mayakan suka kashe jami’an soja sama da 25 lokacin da suke tsaka da sauyawa mutanen wani kauye matsuguni.

Wata majiya ta fadawa jaridar The Cable cewa mayakan na Boko Haram sun shafe sama da sa’o’i uku suna musayar wuta da sojojin a harin na ranar Alhamis.

A cikin wadanda aka kashe a farmakin akwai kwamandan bataliya ta 158 ya yin da wasu daga cikin sojojin ba a san halin da suke ciki ba har ya zuwa lokacin da jaridar ke hada wannan rahoto.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...