Mayaƙan ISWAP 73 sun miƙa wuya ga sojoji a jihar Borno

Mayakan kungiyar ISWAP su 73 tare da iyalinsu ne suka mika kansu ga sojojin shiya ta ɗaya na rundunar Operation Haɗin Kai dake Borno.

A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan al’amuran tsaro da suka shafi yankin tafkin Chadi, 42 daga cikin yan ta’addar tare da iyalinsu da suka haɗa da maza 4 mata 10 da kuma kananan yara 28 da suka fito daga ƙauyukan Bula Bello, Zaramari da kuma Garno sun miƙa kansu a ranar Laraba.

Sojojin bataliya ta 202 dake Bama su ne suka karbe su.

Bayanin na Zagazola ya cigaba da cewa maza biyu da mata 7 da kuma yara 9 daga ƙauyukan Ngauri, Siraja da kuma Nbellana sun miƙa kansu ga dakarun bataliya ta 152.

Zagazola ya kara da cewa mambobin ISWAP 9 da manyan mata biyu daga Ukuba sun miƙa kansu ga rundunar soja dake Gwoza.

Wasu majiyoyi dake rundunar sojan Najeriya ta ce ana cigaba da tantance tsofaffin ƴan ta’addar kafin a miƙa su ga hukumomin da su ka kamata.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Yan sanda sun gano haramtacciyar masana’antar ƙera makamai Cross River

Rundunar yan sandan jihar Rivers ta ce ta bankaɗo wata haramtacciyar masana'antar ƙera bindigogi da nakiyoyi dake garin Osomba a karamar hukumar Akamkpa ta...