Matashiya ta cinna wa kanta wuta a Zamfara saboda soyayya | BBC news

Taswirar Zamfara

Wata matsashiya mai suna Aisha Aminu mazauniyar Albarkatawa a jihar Zamfara ta cinna wa kanta wuta saboda an hana ta auren saurayin da take kauna.

Aisha ta shaida wa BBC cewa ta dauki wannan mataki ne saboda ba za ta iya hakura da shi ba kuma “da ta yi karuwanci gara ta kashe kanta” kawai.

Mahaifin Aisha Aminu Muhammad Albarkawa ya shaida wa BBC cewa saurayi ne take so tsawon shekara daya amma Allah bai sa yana da abin aurenta ba.

“Saboda haka ne muka dakatar da shi da zuwa wurinta tunda ba shi da abin aurenta har sai Allah ya kawo mata wani.,” in ji Aminu Muhammad.

Ya kara da cewa: “Ashe ita kuma tana sonsa sosai. Shi ne ta dauki wannan mataki ba tare da saninnmu ba, kawai sai ganinta muka yi tana ci da wuta, jama’a suka yti kokarin wutar.

“Da aka tambaye ta dalili sai ta ce ita wallahi tana sonsa ne kuma da ta je ta yi iskanci gara ta kashe kanta tun da ba shi da halin da zai iya aurenta.”

Ita ma Aisha ta ce ta dauki wannan mataki ne saboda tana sonsa kuma shi ma yana sonta.

Ta ce: “Na dauki wannan mataki ne saboda ina sonsa kuma tun da muke tare da shi bai taba gaya mani wata magana ba.

“Acaba (okada) yake yi saboda haka sai ya yi zaton cewa ba shi da wani hali. Ni kuma na ce da in je in yi karuwanci gara na kashe kaina na huta kawai. Sai na sa ma kaina fetur kawai, na sa ashana.”

Aisha ta ce ta ji raunuka a hannayenta da bayanta da kuma ciki, sannan kuma ta ce ta yi nadama.

Sai dai ta ce ba ta san halin da masoyin nata yake ciki ba a halin yanzu domin har yanzu bai je dubiya ba.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...