Matar aure yar shekara 15 ta sakawa mijinta shinkafar bera

Rundunar yansandan jihar Kano ta kama wata mata aure mai suna Hassana Lawal yar shekara 15 dake kauyen Beci a karamar hukumar Kumbotso ta jihar.

Ana dai zargin matar ne da sakawa mijinta,mai suna Sale Abubakar dan shekara 33 guba a abinci.

Mai magana da yawun rundunar yansandan jihar,DSP Abdullahi Haruna Kiyawa shine ya tabbatar da kamen cikin wata sanarwa da ya fitar.

Haruna ya ce ranar 16 ga watan Afirilu da misalin karfe biyu na rana rundunar ta samu rahoton dake cewa matar da ake zargi ta bawa mijinta abinci da shinkafar bera a ciki.

An dauki mutumin ya zuwa asibitin kwararru na Murtala Muhammad domin samun kulawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce tuni suka kaddamar da bincike kan lamarin kuma za a gurfanar da wacce ake zargi gaban kotu da zarar an kammala binciken.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...