Rundunar yansandan jihar Kano ta kama wata mata aure mai suna Hassana Lawal yar shekara 15 dake kauyen Beci a karamar hukumar Kumbotso ta jihar.
Ana dai zargin matar ne da sakawa mijinta,mai suna Sale Abubakar dan shekara 33 guba a abinci.
Mai magana da yawun rundunar yansandan jihar,DSP Abdullahi Haruna Kiyawa shine ya tabbatar da kamen cikin wata sanarwa da ya fitar.
Haruna ya ce ranar 16 ga watan Afirilu da misalin karfe biyu na rana rundunar ta samu rahoton dake cewa matar da ake zargi ta bawa mijinta abinci da shinkafar bera a ciki.
An dauki mutumin ya zuwa asibitin kwararru na Murtala Muhammad domin samun kulawa.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce tuni suka kaddamar da bincike kan lamarin kuma za a gurfanar da wacce ake zargi gaban kotu da zarar an kammala binciken.