Matar aure yar shekara 15 ta sakawa mijinta shinkafar bera

Rundunar yansandan jihar Kano ta kama wata mata aure mai suna Hassana Lawal yar shekara 15 dake kauyen Beci a karamar hukumar Kumbotso ta jihar.

Ana dai zargin matar ne da sakawa mijinta,mai suna Sale Abubakar dan shekara 33 guba a abinci.

Mai magana da yawun rundunar yansandan jihar,DSP Abdullahi Haruna Kiyawa shine ya tabbatar da kamen cikin wata sanarwa da ya fitar.

Haruna ya ce ranar 16 ga watan Afirilu da misalin karfe biyu na rana rundunar ta samu rahoton dake cewa matar da ake zargi ta bawa mijinta abinci da shinkafar bera a ciki.

An dauki mutumin ya zuwa asibitin kwararru na Murtala Muhammad domin samun kulawa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ya ce tuni suka kaddamar da bincike kan lamarin kuma za a gurfanar da wacce ake zargi gaban kotu da zarar an kammala binciken.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...