Mataimakin gwamnan jihar Kano ya yi murabus tare da ficewa daga jam’iyar APC ya zuwa PDP

Mataimakin gwamnan jihar Kano, Farfesa Hafiz Abubakar ya sauka daga kan mukaminsa tare da ficewa daga jam’iyar APC inda ya koma jam’iyar adawa ta PDP.

Tsohon mataimakin gwamnan ya kasance makusancin tsohon gwamnan jihar Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya koma jami’yar PDP kwanakin da suka wuce.

Murabus din nasa na bazata baya rasa nasaba da yunkurin tsige shi da wasu yan majalisar dokokin jihar 31 suke shirin farawa a ranar Litinin.

A wata wasika mai dauke da kwanan watan 4 ga watan Agusta wacce ya aikawa gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce yayi murabus din ne saboda ra’ayi mabanbanta da suka gaza cimma dai-dai to akan su.

Abubakar ya ce ya yi iya bakin kokarinsa wajen ganin sun samu dai-daito amma hakan ya ci tura.

A makon da ya gabata ne Abubakar ya sanar da rundunar Æ´ansanda cewa rayuwarsa na fuskantar barazana.

 

 

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...