[ad_1]
Barnabas Bala Bantex, mataimakin gwamnan jihar Kaduna ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar dan majalisar dattawa a zaben shekarar 2019.
Bantex zai tsaya takarar kujerar dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta kudu.
Mazabars ta Kaduna ta kudu da sanata Danjuma Leah yake wakilta ita ce mazaba daya tilo dake ƙarƙashin jam’iyar PDP cikin sanatoci uku dake jihar.
Bayyana takarar ta Bantex zai kawo karshen ce-ce-kucen dake yawo a bakin mutane na cewa gwamna Nasir Ahmad El-rufa’i ba zai sake tsayawa takara tare da shi ba a karo na biyu.
Da yake rokon goyon bayan jama’a, mataimakin gwamnan ya ci alwashin yin wakilci nagari idan har aka zabe shi.
[ad_2]