Mataimakin El-rufa’i zai tsaya takarar sanata

[ad_1]








Barnabas Bala Bantex, mataimakin gwamnan jihar Kaduna ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar dan majalisar dattawa a zaben shekarar 2019.

Bantex zai tsaya takarar kujerar dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta kudu.

Mazabars ta Kaduna ta kudu da sanata Danjuma Leah yake wakilta ita ce mazaba daya tilo dake ƙarƙashin jam’iyar PDP cikin sanatoci uku dake jihar.

Bayyana takarar ta Bantex zai kawo karshen ce-ce-kucen dake yawo a bakin mutane na cewa gwamna Nasir Ahmad El-rufa’i ba zai sake tsayawa takara tare da shi ba a karo na biyu.

Da yake rokon goyon bayan jama’a, mataimakin gwamnan ya ci alwashin yin wakilci nagari idan har aka zabe shi.




[ad_2]

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...