Mata Sun Yi Zanga-Zanga Kan Makomar Zaben Gwamnan Bauchi

Daruruwan mata sun gudanar da zanga zangar lumana a jihar Bauchi jiya Talata, inda suka dirfafi ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC da niyyar toshe kofar shiga hukumar zaben, amma jami’an tsaro da aka jibge don saka ido kan masu kai-komo sun hana matan isa ofishin.

Sai dai jami’an tsaron sun bar matan sun gudanar da zanga zangar ta lumana a dab da kwanar shiga ofishin hukumar zaben.

Wasu daga cikin matan na bayyana cewa sun zabi abinda su ke so amma an hana su, don haka suna mika kukansu da shugaba Muhammadu Buhari, da ya sa a bayyana sakamakon zaben jihar.

Sakataran yada labaran jam’iyyar PDP na Jihar Bauchi, Alhaji Yahaya Nuhu Gabari, ya ce kamar yadda kowa ya sani an yi zaben gwamna ranar 9 ga watan Maris, kuma jam’iyyar PDP ta samu rinjaye wanda ya kamata a tabbatar da wannan zaben cewa, Bala Muhammad Kaura, shi ne ya lashe zaben gwamnan jihar.

Sannan kuma ya yi zargin cewa an yi amfani da wasu dalilai ba bisa ka’ida ba aka ki saka musu kuru’unsu na karamar hukumar Tafawa Balewa.

A martanin da jam’iyyar APC ta mayar ta hannun sakataran kwamitin yada labarai na yakin neman zaben gwamnan jihar, Balarabe Shehu Illela, ya ce matsayin su dan gane da soke zaben, suna da kwarin gwiwar su za su lashe zaben da za a sake gudanarwa.

More News

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...

Hukumar NDLEA ta lalata sama da tan 300 na miyagun kwayoyi da aka kama a Legas da Ogun

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta yi nasarar lalata kilogiram 304,436 da lita 40,042 na haramtattun abubuwa da...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...