Mata Sun Yi Zanga-Zanga Kan Makomar Zaben Gwamnan Bauchi

Daruruwan mata sun gudanar da zanga zangar lumana a jihar Bauchi jiya Talata, inda suka dirfafi ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC da niyyar toshe kofar shiga hukumar zaben, amma jami’an tsaro da aka jibge don saka ido kan masu kai-komo sun hana matan isa ofishin.

Sai dai jami’an tsaron sun bar matan sun gudanar da zanga zangar ta lumana a dab da kwanar shiga ofishin hukumar zaben.

Wasu daga cikin matan na bayyana cewa sun zabi abinda su ke so amma an hana su, don haka suna mika kukansu da shugaba Muhammadu Buhari, da ya sa a bayyana sakamakon zaben jihar.

Sakataran yada labaran jam’iyyar PDP na Jihar Bauchi, Alhaji Yahaya Nuhu Gabari, ya ce kamar yadda kowa ya sani an yi zaben gwamna ranar 9 ga watan Maris, kuma jam’iyyar PDP ta samu rinjaye wanda ya kamata a tabbatar da wannan zaben cewa, Bala Muhammad Kaura, shi ne ya lashe zaben gwamnan jihar.

Sannan kuma ya yi zargin cewa an yi amfani da wasu dalilai ba bisa ka’ida ba aka ki saka musu kuru’unsu na karamar hukumar Tafawa Balewa.

A martanin da jam’iyyar APC ta mayar ta hannun sakataran kwamitin yada labarai na yakin neman zaben gwamnan jihar, Balarabe Shehu Illela, ya ce matsayin su dan gane da soke zaben, suna da kwarin gwiwar su za su lashe zaben da za a sake gudanarwa.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...