Masu zanga-zanga sun yi galaba kan soja a Sudan

Zanga-zangar Sudan

Wasu jiga-jigan gwamnatin mulkin soja su uku a Sudan sun mika tayin sauka daga kan mukamansu- wata muhimmiyar bukata ce ta masu zanga-zanga a kasar.

Ana kallon manyan janar-janar din a matsayin manyan na-hannun daman tsohon shugaba Omar al-Bashir.

Matakin ya zo ne bayan tattaunawa tsakanin sojoji da jam’iyyun adawa kan yadda za a kafa gwamnatin farar hula.

A wani taron manema labarai, kakakin rundunar sojan kasar Laftanar Janar Shamseddine Kabbashi ya ce bangarorin biyu sun cimma matsaya kan mafi yawan bukatun kuma sun yanke shawarar kafa kwamitin hadin gwiwa don warware duk wasu matsaloli.

Jagororin zanga-zanga a Sudan din sun kira wani maci na mutum miliyan daya a yau Alhamis domin matsawa majalisar koli ta sojan kasar mika mulki ga gwamnatin farar hulla.

Jiragen kasa makare da mutane na isa Khartoum, babban birnin kasar don shiga gangamin da za a yi a wajen shelkwatar rundunar soji.

A karon farko, alkalai sun bayyana cewa za su shiga zanga-zangar don nuna goyon bayansu, a cewar kamfanin dillancin labarai na AFP.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...