Masar ce za ta karbi bakuncin Gasar Cin Kofin Afirka a 2019

The Africa Cup of Nations trophy

Wannan karo na biyar da Masar za ta karbi bakuncin gasar

Kasar Masar ce za ta karbi bakuncin Gasar Cin Kofin Kasashen nahiyar Afirka a bana, kamar yadda hukumar da ke kula da harkokin kwallon kafa a nahiyar wato Caf ta bayyana.

Masar ta doke kasar Afirka Ta Kudu, wadda ita ce kasa daya tilo da ta kalubalence ce ta, a wani taron kwamitin zartarwa da aka yi.

Tun da farko an tsara cewa kasar Kamaru ce za ta karbi bakuncin gasar a bana, amma sai aka karbe daga hannunta a watan Nuwambar bara saboda yadda take tafiyar hawainiya wurin gudanar da shirye-shiryen.

Wannan ne karo na biyar da kasar Masar za ta karbi bakuncin gasar, kuma tana da watanni shida kawai kafin fara gasar, wadda a bana kasashe 24 ne za su halarta.

Za a fara gasar ne a watan Yunin bana.

Tun a baya dai hukumar ta Caf ta bai wa kasar Kamaru damar karbar bakuncin gasar shekaru biyu da suka gabata, kuma hakan na nufin an dakatar da wadanda za su karbi bakuncin gasar a shekarun 2021 da 2023 daga shirye-shiryensu.

Yanzu dai hukumar za ta sanar da wadanda za ta karbi bakuncin gasar a ranar Laraba 9 ga watan Janairu.

Kasar Ivory Coast da kuma Guinea wadanda su ne tun farko aka tsara za su karbi bakuncin gasar a 2021 da kuma 2023 sun nuna rashin jin dadinsu da hukuncin da kotun sulhu mai kula da harkokin wasanni ta dauka,

Daga nan, ne sai Guinea ta yanke shawarar dakatar da neman shirya gasar har sai a shekarar 2023.

An sanar da wannan hukunci ne a babban birnin kasar Senegal wato Dakar, wanda a ranar Talata ake sa ran zai karbi bakuncin bikin shekara-shekara inda ake bayar da kyautuka ga gwarazan ‘yan kwallo.

Dan wasan kasar Masar Mohamed Salah na shirin kare kambunsa yayin da zai kara da Pierre-Emerick Aubameyang na kasar Gabon da kuma Sadio Mane na kasar Senegal a matsayin gwarzon dan kwallo na bana.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...