Manhajojin Facebook sun gamu da cikas

Facebook

Kamfanin shafin Facebook na fuskantar matsala mafi tsanani a tarihinsa, inda ake cin karo da matsaloli wajen aiki da wasu daga cikin manhajojinsa na intanet a fadin duniya.

Sai dai kamfanin ya ce yana kokarin shawo kan matsalar.

Baya ga ainahin shafin na Facebook shi kansa, manhajar Messenger da Instagram su ma sun gamu da cikas.

Ba a dai gano abin da ke haddasa matsalar ba, wadda ta fara tun kusan karfe hudu na yamma agogon GMT, wato biyar na yammacin jiya a gogon Najeriya da Nijar.

Masu amfani da shafin Facebook sun iya bude shi amma kuma ba sa iya sanya abubuwa a shafin.

Manhajar Messenger ta waya tana aiki ga wasu amma kuma wasu ba ta yi musu aiki, amma kuma manhajar ta Kwamfutar tebur ba ma a samunta.

Matsalar dai ba ta shafi WhatsApp ba.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...