Man City ta nuna wa Schalke 04 kwanji

Man City

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Manchester City ta yi nasarar doke Schalke 04 da ci 3-2 a wasan farko zagaye na biyu a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Champions League da suka kara ranar Laraba.

City ce ta fara cin kwallo ta hannun Sergio Aguero, daga baya Schalke ta ci biyu duk a bugun fenariti ta hannun Nabil Bentaleb.

Bayan da aka dawo daga hutu ne City ta farke ta hannun Leroy Sane a bugun tazara, sannan Rahem Sterling ya ci na hudu.

City ta kare karawar da ‘yan kwallo 10 a cikin fili, bayan da aka korar mata Nicolas Otamendi a minti na 23 da komawa zagaye na biyu.

Schalke 04 za ta ziyarci Ettihad domin karawa da Manchester City a wasa na biyu a ranar 12 ga watan Maris.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...