Manchester City ta yi nasarar doke Schalke 04 da ci 3-2 a wasan farko zagaye na biyu a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Champions League da suka kara ranar Laraba.
City ce ta fara cin kwallo ta hannun Sergio Aguero, daga baya Schalke ta ci biyu duk a bugun fenariti ta hannun Nabil Bentaleb.
Bayan da aka dawo daga hutu ne City ta farke ta hannun Leroy Sane a bugun tazara, sannan Rahem Sterling ya ci na hudu.
City ta kare karawar da ‘yan kwallo 10 a cikin fili, bayan da aka korar mata Nicolas Otamendi a minti na 23 da komawa zagaye na biyu.
Schalke 04 za ta ziyarci Ettihad domin karawa da Manchester City a wasa na biyu a ranar 12 ga watan Maris.