Man City ta nuna wa Schalke 04 kwanji

Man City

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Manchester City ta yi nasarar doke Schalke 04 da ci 3-2 a wasan farko zagaye na biyu a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Champions League da suka kara ranar Laraba.

City ce ta fara cin kwallo ta hannun Sergio Aguero, daga baya Schalke ta ci biyu duk a bugun fenariti ta hannun Nabil Bentaleb.

Bayan da aka dawo daga hutu ne City ta farke ta hannun Leroy Sane a bugun tazara, sannan Rahem Sterling ya ci na hudu.

City ta kare karawar da ‘yan kwallo 10 a cikin fili, bayan da aka korar mata Nicolas Otamendi a minti na 23 da komawa zagaye na biyu.

Schalke 04 za ta ziyarci Ettihad domin karawa da Manchester City a wasa na biyu a ranar 12 ga watan Maris.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...