Man City ta nuna wa Schalke 04 kwanji

Man City

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Manchester City ta yi nasarar doke Schalke 04 da ci 3-2 a wasan farko zagaye na biyu a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Champions League da suka kara ranar Laraba.

City ce ta fara cin kwallo ta hannun Sergio Aguero, daga baya Schalke ta ci biyu duk a bugun fenariti ta hannun Nabil Bentaleb.

Bayan da aka dawo daga hutu ne City ta farke ta hannun Leroy Sane a bugun tazara, sannan Rahem Sterling ya ci na hudu.

City ta kare karawar da ‘yan kwallo 10 a cikin fili, bayan da aka korar mata Nicolas Otamendi a minti na 23 da komawa zagaye na biyu.

Schalke 04 za ta ziyarci Ettihad domin karawa da Manchester City a wasa na biyu a ranar 12 ga watan Maris.

More News

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...

Hukumar NDLEA ta lalata sama da tan 300 na miyagun kwayoyi da aka kama a Legas da Ogun

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta yi nasarar lalata kilogiram 304,436 da lita 40,042 na haramtattun abubuwa da...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...