Majalisar wakilai ta amince Buhari ya nada masu bashi shawara 15

Majalisar wakilai ta tarayya ta amince da bukatar da shugaban kasa Muhammad Buhari ya aika mata dake neman a sahale masa ya nada masu bashi shawara 15.

Sahalewar ta biyo bayan amincewa da majalisar tayi da kudurin shugaban masu rinjaye,Alahsan Ado Doguwa ya gabatar a zauren majalisar ya yin zamanta na ranar Alhamis.

Yin hakan da majalisar tayi ya yi dai-dai da sashe 151(1) na kundin tsarin mulkin Najeriya na shekarar 1999.

Sashen ya ce shugaban kasa nada ikon ya nada kowane mutum a matsayin mai bashi shawara domin ya taimaka masa wajen gudanar da ayyukansa.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya,NAN ya rawaito cewa shugaban kasar a wani sako da ya aikewa majalisar ranar 9 ga watan Yuli ya nemi sahalewar majalisar domin ya nada mutane masu bashi shawara 15

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...