Majalisar malamai ta yi watsi da sakamakon zaben Kano

Majalisar malamai ta jihar Kano ta yi watsi da zaben gwamnan jihar da aka sake a ranar Asabar, 23 ga watan Maris, ta bayyana shi a matsayin fashin damokradiyya.

A wani jawabi dauke da sa hannun Dr. Yusuf Ibrahim Kofar Mata, Shugaban kungiyar, yace majalisar malamai ta Kano sun yi Allah wadai sannan sun yi watsi da fashin damokradiyya da mutanen Kano suka fuskanta a kwanan nan, da sunan zaben gwamna.

Dr. Kofar Mata ya bayyana cewa,
“kamar kowane mai son zaman lafiya a Kano, masu kula da zabe da dama na gida da wajen kasar sun yi korafin cewa zaben wanda ya kamata ya zama na gaskiya da amana, da kuma zaman lafiya ya zamo cike da karya doka.”

Majalisar malaman a cikin jawabin ta jero tarin karya doka da aka yi kamar haka: “tarin siyan kuri’u daga yan siyasar APC, yaduwar rikici wanda jam’iyya mai mulki ta shirya kuma ta dauki nauyi domin razanarwa da kuma tozarta masu zabe da jami’an PDP.”

Har ila yau majalisar tayi korafi akan yadda aka wofantar da na’urar tantance katunan zabe, wanda a cewarta hakan kwace yancin masu zabe ne da kuma hadn bakin jami’an INEC da wasu hukumomin tsaro.

Daga karshe sun yi kira ga gwamnatin tarayya da dukkanin hukumomin da abun ya shafa, da su yi kokarin kwato wa mutane yancinsu domin tabbatar da damokradiyyar kasar.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...