Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta ki tantance wani a matsayin kwamishina saboda rubutu a Facebook

Yayin zamanta na yau domin tantance sabbin Kwamishinoni, majalissar dokokin jihar Kaduna ta ki tantance Alhaji Aliyu Jaafaru a matsayin sabon Kwamishinan Noma Na jihar da gwamna Mallam Nasiru El-Rufai ya bada sunansa saboda wani rubutu dayayi na sukar Gwamnatin Jihar Kaduna akan tsarin tantance malaman makaranta da Gwamnatin tayi a shekarar 2017.

Alhaji Aliyu Jaafaru yazo zauren majalissar tun kafin shugaban majalissar ya iso, sai dai kuma bai samu tantancewa ba bayan da shugaban majalissar Alhaji Aminu Shagali yayi masa tuni akan rubun sukar Gwamnatin Jihar Kaduna dayayi a shekarar 2017 akan tsarin tsaftace Ilimi.

Shagali yace “A rubutunka da kayi a kafar sadarwar Facebook a shekarar 2017 ka soki Gwamnatinmu a bainar Jama’a inda ka bayyana Gwamnatinmu bamaison cigan jihar Kaduna bace”.

Shagali ya kara da cewa kayi rubutu kala-kala akan yunkurin Gwamnatin mu na tsaftace Ilimi”.

Daga karshe Shagali yadan bayyanawa Alhaji Jaafaru Irin rubutun da yayi a wancan lokacin inda yaki bada umarnin tantanceshi saboda rubutun dayayi a wancan lokacin.

Daga yake karin haske akan lamarin shugaban kwamitin majalissar akan harkokin sadarwa da yada labarai Alhaji Tanimu Musa ya bayyanawa manema labarai cewa anki tantance Alhaji Aliyu Jaafaru saboda ya kalubalanci Gwamnatin Mallam Nasiru El-Rufai a kafar Facebook a shekarar 2017.

Daga cikin kwamishinonin da aka tantance akwai Kwamishinan Tsare-tsare Mr Thomas Gyang, kwamishinan Fadar Gwamnati da Gyare-gyare Hassan Mahmud, sai mai binciken kudi Alhaji Atiku Musa inda majalissar ta bukaci daya fara binciken asusun kananan hukumomi nan take sai matemakiyar Gwamna a matsayin mukaddashin Kwamishiniyar Lafiya.

ZTH

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...