Majalisar dokokin Jigawa ta dakatar da shugabannnin ƙananan hukumomi uku

Majalisar dokokin jihar Jigawa ta dakatar da wasu shugabannin ƙananan hukumomi uku kan zargin yin tafiya kasar waje ba tare da izinin majalisar dokokin jihar ba da na bangaren zartarwa.

Shugabannin da aka dakatar sun haÉ—a da Mubarak Ahmad na Æ™aramar hukumar Birniwa sai Rufa’i Sanusi na Gumel da kuma Umar Baffa na Æ™aramar hukumar Ƴankwashi.

Ana zargin shugabanni uku ne da tafiya kasar Rwanda ba tare da izini ba.

Majalisar ta ɗauki matakin ne bayan da shugaban kwamitin ƙananan hukumomi, Aminu Zakari Tsubut ya gabatar da kudirin dakatar da shugabannnin.

Ya ce gabanin tafiyarsu majalisar ta bayar da umarni ga shugabannin ƙananan hukumomi da kada su yi tafiya ko ina saboda shirye-shiryen kasafin kuɗin shekarar 2024 da kuma gabatar da shi gaban majalisar da gwamna zai yi.

Har ila yau majalisar ta kafa kwamiti karkashin shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Muhammad Dansure da ya gudanar da bincike kan lamarin kana ya miƙa rahoto cikin makonni huɗu.

More News

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama Æ´an kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan Æ´an sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan Æ´an...

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto. Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da...

Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman. Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake...