Majalisar Dattawan Najeriya ta shigar da kara a kotun kolin kasar kan batun dakatar da Babban Alkalin kasar.
Majalisar wadda ta yi niyyar zama a ranar Talata 29 ga watan Janairu, ta dage zaman saboda karar da ta shigar.
A sanarwar da jami’in hulda da jama’a na Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya ya fitar Yusuph Olaniyonu a shafin ofishin shugaban majalisar dattawa na Twitter, ta bayyana cewa sun shigar da karar ne a kotun koli.
Suna neman kotun ne da ta yi masu bayani a kan ko shugaba Buhari na da hurumin cire Mista Onnoghen.
Sanarwar ta bayyana dage zaman da aka shirya yi a ranar Talata saboda dama a kan batun cire Onnoghen za a yi.
A halin yanzu tunda batun na a gaban kotu sun fasa zaman saboda ba a tattauna batu idan yana a gaban kotu.
Cire Alakalin Alakalan Najeriya da Buhari ya yi na ci gaba da jawo ce-ce-ku-ce daga cikin Najeriya da kuma wajen kasar, inda kan lauyoyin kasar ya rabu, wasu na goyo baya wasu na Allah-wadai.
Fadar shugaban kasa ta daure fuska kan rashin jin dadin al’amarin da Amurka da Birtaniya suka nuna, inda ta bayyana cewa ba za ta amince da katsalandan daga kasashen waje ba.