Mai shari’a Walter Onnoghen ya daukaka kara

Justice Walter Onnoghen

Hakkin mallakar hoto
AFP

Image caption

Wannan shi ne karon farko da aka gurfanar da Alkalin Alkalai a Najeriya a gaban kotu aka kuma yanke masa hukunci

Tsohon Babban Mai shari’a na Najeriya na baya bayan nan Justice Walter Onnoghen ya daukaka kara a kan hukuncin da kotun da’ar ma’aikata ta yanke masa kan laifin kin bayyana biyar daga cikin asusun bankunansa wadanda ke dauke da tarin kudaden waje.

Onnoghen ya gabatar da korafe-korafe guda 16 a gaban kotun daukaka karar a Abuja, jim kadan bayan da kotun da’ar ma’aikatan ta yanke masa hukunci ranar Alhamis.

A daya daga cikin korafe-korafen da ya gabatar ya kafe cewa bai taba amsa laifin cewa ya aikata laifukan da kotun ta zarge shi da su ba, kamar yadda kotun da’ar ma’aikatan ta ce.

Takardar daukaka karar ta kara da cewa, ”Mai daukaka karar (onnoghen) bai amsa laifin kin bayyana dukiyarsa ba daga shekara ta 2005 a matsayinsa na mai shari’a na kotun koli.

”Mai daukaka karar kawai ya bayyana cewa bai bayyana ba ne a shekara ta 2009 kamar yadda aka bukata, saboda ya manta, kuma nan da nan ya bayyana bayan da ya gano hakan.”

Justice Onnoghen ya kuma ce kotun da’ar ma’aikatan ta yi kuskure a tsarin shari’a, kan korar korafin da ya shigar na kalubalantar ikonta na yi masa shari’a, wanda hakan ya keta haddin shari’a.

Haka kuma ya ce kotun ta yi kuskure a tsarin shari’a, kan korar bukatarsa da ta yi wadda a ciki ya nemi alkalin kotun da ya dakatar da yi masa sharia’a bisa zargin nuna bambanci ko san zuciya.

Hakkin mallakar hoto
Reuters

Image caption

Lauyoyi masu kare Justice Walter Onnoghen a yayin wani zama na kotun da’ar ma’aikata

A takardar daukaka karar, Justice Onnoghen ya gabatar da bukatar kotun daukaka karar ta bayar da damar sauraran karar da ya daukaka, sanna kuma ta yanke hukuncin cewa kotun da’ar ma’aikatan ba ta da hurumin sauraren wannan shari’a tasa.

Bugu da kari ya bukaci kotun daukaka karar ta yi watsi da hukuncin da waccan kotun ta yi masa, kana ta wanke shi kuma ta sallame shi, baya ga wasu bukatun kuma.

Ita dai kotun da’ar ma’aikatan ta samu Mai shari’a Onnoghen da laifi, ta kuma cire shi daga mukamin babban mai shari’a na Najeriya, da kuma mukamin shugaban hukumar da’ar ma’aikata(CCB).

Haka kuma ta haramta masa rike wani mukami na gwamnati a tsawon shekara 10, baya ga umartarsa da ya mika dukkanin asusun banki biyar wadanda bai bayyana mallakarsu ba a tsakanin 2009 da 2015.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Wasu sun yi zargin cewa shari’ar ta Onnoghen tana da alaka da siyasa, saboda an fara ta ne gab da babban zaben kasar

Dakatar da Onnoghen a can baya ya jawo ce-ce-ku-ce da dama a Najeriya, inda har kungiyar lauyoyin kasar ta yi zanga-zanga kan matakin da Shugaba Buhari ya dauka kan Mista Onnoghen.

Kungiyar ta bukaci mambobinta da su kaurace wa kotu har na tsawon kwana biyu, umarnin da wasu suka bi wasu kuma suka yi burus da shi.

Haka kuma a lokacin dakatarwar, babbar jam’iyyar hamayya ta PDP da kasashen Amurka da Birtaniya da kuma Tarayyar Turai sun yi Allah-wadai da dakatar da shi.

Shugaba Buhari dai ya dakatar da Mista Onnoghen ne bisa shawarar kotun da’ar ma’aikata wacce ta same shi da laifin kin bayyana cikakkun kaddarorinsa lokacin da aka nada shi mukamin alkalin alkalan a shekarar 2017.

An zargi Shugaba Buhari da katsa-landan a harkokin shari’a saboda gurfanar da Onnoghen a kotun, ko da za a kalubalanci sakamakon zabensa a kotun koli, inda ake ganin Onnoghen a matsayin barazana ga nasarar ta Buhari idan yana kan matsayinsa na Babban Mai shari’a na kasar.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...