[ad_1]
Bolaji Abdullahi ya sauka daga kan mukaminsa na mai magana da yawun jam’iyar APC.
Ajiya Talata ne ya musalta rahotanni dake cewa ya fice daga jam’iyyar biyo bayan fitar sanata Bukola Saraki daga jam’iyar.
Amma a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, ya ce yanke shawarar ficewa daga jam’iyar saboda yadda a a kullum ake nuna shakku kan biyayyarsa ga jam’iyar.
Abdullahi ya bayyana cewa ruguje shugabancin jam’iyar na jihar Kwara ya nuna yadda kwamitin zartarwar uwar jam’iyar ya ɗauki bangaranci hakan ya saba da rantsuwar da suka yi ta gudanar da aiki.
[ad_2]