Mako hudu ke nan tunda gwamnatin Amurka, karkashin Donald Trump, ta rufe wasu ofisoshin gwamnati a fadin kasar.
Wannan lamarin ya janyo dakatar da ayyukan gwamnati, lamarin da ya shafi ayyukan yau da kullum, kuma ma’aikata da dama basa samun albashi.
Ma’aikata dubu dari takwas matsalar ta shafa, kuma shugaban Amurkan ya yi kashedin zai sake daukar wasu matakan idan majalisar kasar ba ta mika masa kudden gina wat katang a kan iyakar kasar da Mexico ba
Rabon da Amurkawa su ga irin wannan matsalar dakatar da ayyukan gwamnati tun 1995 lokacin mulkin Bill Clinton inda majalisar kasar a karkashin jagorancin kakakinta Newt Gingrich suka kasa cimma matsaya.
Wannan takardamar ta yanzu da aka fara kwana hudu kafin bikin Kirsimeti kawo yanzu, ya shiga kwana na 22 – kuma shi ne mafi tsawo a tarihin siyasar kasar.
Batun da ya janyo wannan takardamar shi ne na gina wata katanga da shugaba Trump ya ce zai rage kwararar makamai da hodar iblis da kuma kungiyoyin masu aikata manyan laifuka daga shiga kasar ta iyakar ksar da Mexico.
Kin amincewar da ‘yan jam’iyyar Demokrat suka yi na sakin baitulmalin kasar ga shugaba Trump ya harzuka shi, inda ya yi gargadin zai yi shelar ko ta baci.
Dubban daruruwan ma’aikatan gwamnati sun ci gaba da zuwa wajen aiki babu albashi.
Ma’aiktan sun hada da jami’ian tsaro a filayen jiragen saman kasar, da kuma jami’an hukumar FBI mai binciken manyan laifuka.
Duk da kiraye-kirayen da Mista Trump ke yi na ‘yan jam’iyyar Demokrat su hau teburin tataunawa, babu alamar hakan zai samu.