Kuskure ne a bari PDP ta dawo karagar mulkin Najeriya

Tsohon shugaban hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya, Malam Nuhu Ribadu, bayyana fargabar cewa dawowar jam’iyyar adawa ta PDP karagar mulki zai iya kawo matsaloli baya ga abin da ya ce gagarumar nasarar da aka samu a fannin yaki da cin hanci.

Ribadu wanda shi ne babban jami’in tuntunba na kamfen din ta-zarcen shugaba Muhammadu Buhari, ya ce aikin yaki da cin hanci da gwamnatin APC ta yi, ya fi duk abin da PDP ta gudanar a tsawon shekaru 16 da ta yi tana mulki.

“Ka ga mutum shi kadai, duk duniya yana da gida a ko ina, kana da shi a Ingila kana da shi a America, kana da shi a Dubai. Mutumin da ya yi shekara uku ya zo ya kawo canji a rayuwarmu, za ka ce in cire shi, in dawo da wanda ya yi min lalaci, duk irin nadamar da ya yi, ai ni ba wawa ba ne.” inji Ribadu.

Kalaman nasa na zuwa ne kwanakin kadan kafin ‘yan Najeriya su yi zaben shugaban kasa.

Sai dai babbar jam’iyyar adawa ta PDP, ta ce, kushe ta da APC ke yi, alamu ne na rashin adalci da kuma rashin hujjar rashin cika alkawuran kamfen da hakan ya jefa ‘yan Najeriya cikin kunci.

“A kasar nan, babu tsaro, babu abinci, babu ayyuka, tattalin arzikin kasa ya lalace, matasa sai shaye-shaye, kai har harkokinmu da kasashen waje ya tabu. To idan aka ce wannan gwamnati ta komo ta sake shekara hudu, sai mu ce Najeriya Allah ya sawwake in akwai ta.” Inji Sakataren PDP na kasa, Sanata Umar Tsauri.

Tuni dai hukumar zabe ta fara tura kayayyakin zabe da hakan ke nuna ba damuwar dage zaben kamar yadda aka gani a 2015.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...

Sojoji a birnin Ibadan  sun kama Æ´an fafutukar kafa Æ™asar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo. Masu fafutukar sanye da...