Kuskure ne a bari PDP ta dawo karagar mulkin Najeriya

Tsohon shugaban hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya, Malam Nuhu Ribadu, bayyana fargabar cewa dawowar jam’iyyar adawa ta PDP karagar mulki zai iya kawo matsaloli baya ga abin da ya ce gagarumar nasarar da aka samu a fannin yaki da cin hanci.

Ribadu wanda shi ne babban jami’in tuntunba na kamfen din ta-zarcen shugaba Muhammadu Buhari, ya ce aikin yaki da cin hanci da gwamnatin APC ta yi, ya fi duk abin da PDP ta gudanar a tsawon shekaru 16 da ta yi tana mulki.

“Ka ga mutum shi kadai, duk duniya yana da gida a ko ina, kana da shi a Ingila kana da shi a America, kana da shi a Dubai. Mutumin da ya yi shekara uku ya zo ya kawo canji a rayuwarmu, za ka ce in cire shi, in dawo da wanda ya yi min lalaci, duk irin nadamar da ya yi, ai ni ba wawa ba ne.” inji Ribadu.

Kalaman nasa na zuwa ne kwanakin kadan kafin ‘yan Najeriya su yi zaben shugaban kasa.

Sai dai babbar jam’iyyar adawa ta PDP, ta ce, kushe ta da APC ke yi, alamu ne na rashin adalci da kuma rashin hujjar rashin cika alkawuran kamfen da hakan ya jefa ‘yan Najeriya cikin kunci.

“A kasar nan, babu tsaro, babu abinci, babu ayyuka, tattalin arzikin kasa ya lalace, matasa sai shaye-shaye, kai har harkokinmu da kasashen waje ya tabu. To idan aka ce wannan gwamnati ta komo ta sake shekara hudu, sai mu ce Najeriya Allah ya sawwake in akwai ta.” Inji Sakataren PDP na kasa, Sanata Umar Tsauri.

Tuni dai hukumar zabe ta fara tura kayayyakin zabe da hakan ke nuna ba damuwar dage zaben kamar yadda aka gani a 2015.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...