Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Dokar Wa’azi a Kaduna

VOA Hausa

Sheik Halluru Maraya daya ne daga cikin manyan malaman addini musulunchi a Kaduna, kuma ya ce kamata ya yi gwamnati ta yi dokoki kan satar mutane ba wa’azi ba.

Ita ma kungiyar Kiristochi ta Nigeriya CAN ta ce hukuncin ya yi mata daidai. Rev. Joseph John Hayap shine shugaban kungiyar a Kaduna, ya ce tun farko suma sun yi niyar shigar da ‘kara amma lauyansu ya ce ‘kara ‘daya da aka shigar ya isa.

To sai dai mai taimakawa gwamnan jihar Kaduna ka harkokin addinin musulunci, Sheik Jamil Abubakar Albani, ya ce akwai kuskuren fahimta game da wannan doka, kasancewa har yanzu ba ta kai ga mai girma gwanan jihar Kaduna ba, kafin ya yi nazarinta domin matakin da zai ‘dauka.

Dama dai tun bayan kai wannan kudurin dokar wa’azi gaban Majalissar Dokokin Kaduna a shekarar 2016, darikar Fentacostal ta shigar da kara gaban babar kotun Kaduna wanda a ranar Laraba nan alkaliyar kotun mai Shari’a Hannatu Gwadah ta yanke hukuncin cewa kudurin ya sabawa kundin dokar kasa na 1999.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...