[ad_1]
Wata babbar kotu dake jihar Sokoto ta wanke tsohon gwamnan jihar, Attahiru Bafarawa daga zargin aikata laifin cin hanci da rashawa.
Hukumar Yaki Da Yiwa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati EFFC ce ta gurfanar da shi a gabanta inda take zarginsa da aikata almuundahanar kudade.
Sauran waÉ—anda kotun ta wanke sun haÉ—a da kamfanonin Beedash Nigeria Limited, Nasdabap Nigeria Limited, da wasu mutane biyu Nasiru Dalhatu Bafarawa da kuma Salihu Maibuhu Gummi.
EFCC ta zargi Bafarawa da yin almubazzaranci da kuma almuundahanar kudaden gwamnati, a tsakanin shekarar 1999-2007 lokacin da yake kan kujerar mulkin gwamnan jihar.
Bello Abbas, alkalin dake sauraran shari’ar ya yi watsi da dukkanin tuhume-tuhumen da EFCC kewa Bafarawa da kuma mutane, alkalin ya ce hukumar ta gaza gabatar da kwararan hujjoji da za su tabbatar da laifin.
Hukumar ta yi watsi da hukuncin kotun inda tace zata daukaka kara.
[ad_2]