Ko Man City za ta iya kafa tarihin cin kofuna hudu?

Raheem Sterling na murnar cin kofin Carabao da Manchester City ta yi

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Manchester City ta doke Chelsea 4-3 a fanareti ta ci kofin Carabao a watan Fabrairu

Manchester City ta je gidan Fulham a wasan gasar Premier ranar Asabar din nan cike da sanin cewa wasa 15 ya rage ma ta da kafa tarihin cin kofuna hudu a kaka daya.

Bayan da tuni ta riga ta dauki kofin League, maki daya ne tsakaninta da Liverpool wadda ke mara ma ta baya a Premier, da kuma kwantan wasa daya, yayin da za ta fuskanci Brighton a wasan kusa da karshe na kofin FA, sannan kuma ta fafata da Tottenham a wasan dab da na kusa da karshe a gasar kofin Zakarun Turai.

Bugu da kari kuma masu fashin-baki na ganin kungiyar tana da dama da karfin cin dukkanin wadannan kofuna da ke gabanta a yanzu.

To amma za ta iya tabbatar da wannan hasashe kuwa?

Akwai wata kungiya da a tarihi ta taba samun irin wannan dama kuwa?

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Ana ganin bajintar Man United ta cin kofuna uku a kakar 1998-99 ita ce mafi girma a Ingila

Kungiyoyin Ingila biyu ne kawai suka taba samun irin wannan dama ta cin kofuna hudu zuwa ranar 30 ga watan Maris: Chelsea a kakar 2006-07, da Manchester United a 2008-09.

Chelsea wadda a lokacin Jose Mourinho ke ma ta kociya ta kasance da wannan dama har zuwa 1 ga watan Mayu, kafin ta yi rashin nasara a bugun fanareti a karawarta da Liverpool a wasan kusa da karshe na kofin Zakarun Turai.

Shekara biyu bayan nan Manchester United karkashin Sir Alex Ferguson ta yi kokari har zuwa ranar 19 ga watan Afrilu, kafin ta gamu da karshen wannan fata, bayan da Everton ta yi waje da ita a bugun fanareti a wasan kusa da karshe na kofin FA.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Riyad Mahrez ne ya ci wa Man City kwallo daya tilo da ta doke Tottenham a Premier a Oktoba

Manchester United din harwayau ta kai matakin kusan daukar cin kofunan hudu, kafin ta sha kashi a hannun Barcelona a wasan karshe na cin kofin Zakarun Turai.

Bajintar da za a ce United din ta yi da ta fi kowacce a tarihinta ita ce ta cin kofuna uku daga cikin hudun a kakar 1998-99, amma ina ko alama ba ta kai ga kusan daukar hudun ba a wannan kaka, inda ta yi rashin nasara a hannun Tottenham a wasan dab da na kusa da karshe na kofin League ranar 2 ga Disamba.

Wata gwarzuwar kungiyar ta Premier, ita ce tawagar Arsenal da aka yi wa lakabi da ‘invincibles’ ta kakar 2003-04.

Tawagar ta kafa tarihin ganin ba wata kungiya da ta doke ta a wannan kaka a gasar Premier, amma burinta na daukar kofunan hudu a kaka daya ya zo karshe ranar 3 ga Fabrairu, lokacin da suka sha kashi da ci jumulla 3-1 da Middlesbrough a wasan kusa da karshe na kofin League.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Pep Guardiola na fatan kafa wa Manchester City tarihin daukar kofuna hudu a kaka daya, abin da ba a taba yi ba a Ingila

Tawagar Manchester City, wadda ta yi ta kawar da tarihin da aka kafa a baya a Premier a wajen yawan maki da kuma cin yawan kwallo, a kan hanyarta ta daukar Premier a bara, tana fafatawa a fagen daukar kofuna hudu har zuwa ranar 19 ga watan Fabrairu, kafin ta gamu da rashin nasara a hannun Wigan a kasar cin kofin FA.

To amma babbar bajinta da City din ta yi kafin wannan shekarar ta kasance ne a kakar 2013-14, lokacin ta kungiyar karkashin Manuel Pellegrini ta sha kashi a wasan dab da na kusa da karshe na kofin FA ranar 9 ga watan Maris, harwayau a hannun Wigan. Saboda haka a iya cewa kungiyar ta ci sa’a da ba za ta hadu da Wigan din ba a bana.

Yanzu dai ba a san ko Manchester City za ta yi wannan bajinta da ta gagara ba a Ingila.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...