Dan wasan tsakaiya na Manchester City evin de Bruyne gwaji ya tabbatar da ya kamu da cutar korona bayan ya dawo daga buga wa ƙasarsa Belgium wasa.
Ɗan wasan mai shekara 30 ya killace kansa na tsawon kwana 10, wanda hakan ke nufin ba zai buga wasan da Manchester City za ta kara da Everton ba a ranar Lahadi da kuma karawar gasar zakarun Turai da Paris St-Germain.
De Bruyne, wanda aka yi allurar rigakafin korona, ya ci wa Belgium ƙwalli a wasan neman gurbin gasar cin kofin duniya ƙasarsa ta fafata da Wales a ranar Talata.
“Muna fatan alamomin ba su yi muni ba,” in ji kocinsa Pep Guardiola.
“Ba za a daɗe ba zai dawo, ba za mu damu da irin girman giɓin da muka samu ba. Yana da muhimmanci sosai. Dole mu taimaka masa kuma muna fatan zai samu sauƙi a yayin da ya killaci kansa.”
(BBC Hausa)