Kevin de Bruyne: Ɗan wasan tsakiya na Manchester City ya kamu da Covid-19

Kevin de Bruyne celebrates scoring for Belgium

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto,
Kevin de Bruyne scored for Belgium on Tuesday

Dan wasan tsakaiya na Manchester City evin de Bruyne gwaji ya tabbatar da ya kamu da cutar korona bayan ya dawo daga buga wa ƙasarsa Belgium wasa.

Ɗan wasan mai shekara 30 ya killace kansa na tsawon kwana 10, wanda hakan ke nufin ba zai buga wasan da Manchester City za ta kara da Everton ba a ranar Lahadi da kuma karawar gasar zakarun Turai da Paris St-Germain.

De Bruyne, wanda aka yi allurar rigakafin korona, ya ci wa Belgium ƙwalli a wasan neman gurbin gasar cin kofin duniya ƙasarsa ta fafata da Wales a ranar Talata.

“Muna fatan alamomin ba su yi muni ba,” in ji kocinsa Pep Guardiola.

“Ba za a daɗe ba zai dawo, ba za mu damu da irin girman giɓin da muka samu ba. Yana da muhimmanci sosai. Dole mu taimaka masa kuma muna fatan zai samu sauƙi a yayin da ya killaci kansa.”

(BBC Hausa)

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...