Kawunan masana shari’a ya rabu kan zaben Kano

Manyan 'yan takarar kujerar gwamna a Kano

Hukumar INEC ta ce za a sake zabukan ne wasu mazuka a ranar 23 ga watan Maris

Jihar Kano ta shiga jerin gwanon jihohin da INEC ta bayyana cewa ba a kammala zaben ta ba, jihohin da suka hada da Adamawa da Benue da Sokoto da Bauchi da kuma Plateau.

Barister Bulama Bukarti da Barrister Mai Nasara Kogo Umar sun bayyana mabambantan ra’ayoyi game da batun rashin bayyana wadanda suka lashe zabe a wadannan jihohi.

Bukarti ya ce bai kamata a soke zaben wadannan jihohin ba, yayin da Barrister Kogo yake ganin akwai hujjoji masu karfi da suka sa hukumar INEC ta ki bayyana sakamakon zabukan.

Bukarti a nasa ra’ayin yana ganin cewa akwai yiyuwar kotu ta saurari jam’iyyar da ke korafi game da matakin, wata kila ma kotu ta tabbatar musu da nasararsu. ba tare da an sake zabe ba.

Na’urarku na da matsalar sauraren sauti

Tattaunawar Barister Bulama Bukarti da Barrister Mai Nasara Umar kan batun zaben

Kun san jihohin da INEC ta kammala zaben gwamna?

Jerin jihohin da INEC ta bayyana zabensu a matsayin wanda aka kammala:

  • Abia – Okezie Ikpeazu (PDP)
  • Akwa Ibom – Udom Emmanuel (PDP)
  • Borno – Babagana Umara Zulum (APC)
  • Cross River – Ben Ayade (PDP)
  • Delta – Govnor Ifeanyi Okowa (PDP)
  • Ebonyi – David Umahi (PDP)
  • Enugu – Ifeanyị Ugwuanyi (PDP)
  • Gombe – Alhaji Inuwa Yahaya (APC)
  • Imo – Emeka Ihedioha (PDP)
  • Jigawa – Mohammadu Badaru Abubakar (APC)
  • Kaduna – Govnor Nasir El-Rufai (APC)
  • Katsina – Aminu Masari (APC)
  • Kebbi – Abubakar Atiku Bagudu (APC)
  • Kwara – Abdulrahman Abdulrazaq (APC)
  • Lagos – Babajide Olusola Sanwo-Olu (APC)
  • Nasarawa – Abdullahi Sule (APC)
  • Niger – Govnor Abubakar Bello (APC)
  • Ogun – Prince Dapo Abiodun (APC)
  • Oyo – Seyi Makinde (PDP)
  • Taraba – Darius Ishaku (PDP)
  • Yobe – Alhaji Mai Mala Buni (APC)
  • Zamfara – Muktar Idris (APC)

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...