Kannywood na kan hanyar durkushewa – Zaharadden

Zaharadden Sani

Hakkin mallakar hoto
Facebook/Zaharadden

Daya daga cikin fitattun masu shirya fina-finan Hausa a Najeriya ya yi kira ga gwamnatin kasar da ta kai musu daukin gaggawa domin hana harkar fina-finan na Kannywood durkushewa.

Zaharadden Sani ya ce Kannywood ya kama hanyar durkushewa kurmus, kuma tallafin hukumomi ne kawai zai iya tserar da su.

“A yanzu babu riba a harkar fim, asara muke yi… Yawancin jarumai na rige-rigen kafa wasu sana’o’in daban,” in ji shi.

Akwanakin nan dai wasu manyan jaruman Kannywood sun kara bazama wurin fadada hanyoyin samun kudadensu.

Jarumi Ali Nuhu ya bude wani shagon sayar da kaya a Kano, yayin da Sani Danja da Yakubu Muhammad suka bude gidan hoto.

Zaharadden ya ce: “Na samu labarin cewa gwamnati na shirin yin wani abu kan wannan matsalar, amma ina bayar da shawarar cewa ka da a tallafawa tsirarun mutane domin hakan ba zai kawar da matsalar ba sai dai ya azirta wasu ‘yan kalilan”, kamar yadda ya shaida wa Premium Times.

Ya kara da cewa duk lokacin da aka bayar da kudi irin wadannan, “to wasu mutane ne kawai za su wawure domin amfanin kansu”.

Sannan ya yi kira da gwamnati da ta gina gidajen kallon fim a arewacin kasar.

Tuni dama jarumai mata kamar Rahama Sadau da Hadiza Gabon suka fara sayar da kayayyakin kwalliya da kuma yin tallace-tallace ga kamfanoni.

Yayin da wasu kuma kamar su Adam A Zango suka kara kaimi a fagen waka da kuma shirya tarukan wakoki musamman a lokutan bukukuwa kamar na sallah da sauransu.

Da ma wasu masu sharhi sun fara alakanta irin wannan fadada harkokin da wasu jaruman ke yi da karancin armashin da fina-finan suke kara yi.

Zaharadden ya ce a yanzu aikinsu shi ne su shirya fim su sayar ga DSTV ko Arewa TV, saboda babu riba.

“Na shirya fim (Abu Hassan) kwanaki, inda na tafka asara saboda na kashe kudade amma na buge da sayar da shi ga DSTV a arha. Wannan shi ne abin da muke yi yanzu,” in ji jarumin, wanda har ila yau ya kware wurin shirya fina-finai.

Masu shirya fim sun dade suna kokawa kan satar fasahar da suka ce ana yi musu.

Sannan kuma a yanzu suna fuskantar barazana daga fina-finan China da Amurka da Turkiyya da ake fassara wa zuwa harshen Hausa, kuma ake samunsu a tashoshin tauran da’adam cikin sauki.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...