Wani dan sanda na tafiya a gefen wata mota da masu goyon bayan shugaban Kungiyar ‘Yan Uwa Musulmi, Sheikh Ibrahim Zakzaky suka kona a kusa da harabar majalisar dokokin Najeriya a Abuja, babban birnin kasar ranar 9 ga watan Yulin 2019.
Masu goyon bayan shugaban ‘yan Shi’an da ke tsare sun yi arangama da jami’an tsaro kuma mutane da yawa sun samu raunuka ciki har da ‘yan sanda biyu kamar yadda hukumomi da shaidu suka bayyana.
‘Yan kwana-kwana na kokarin kashe wutar da ke fitowa daga wata mota bayan arangamar tsakanin jami’an tsaro da magoya bayan Sheikh Ibrahim Zakzaky.
Mummunar arangamar ta jikkata mutane. Wani takalmi a wurin da jini ya zuba yayin rikicin tsakanin jami’an tsaro da mabiya Ibrahim Zakzaky.
An lalata motoci da gine-gine a lokacin taho-mu-gaman. Nan wani wurin tsayuwar ‘yan sanda ne da masu zanga-zangar suka lalata ranar 9 ga watan Yulin 2019.
Kungiyar ‘Yan Uwa Musulmin dai sun musanta zarge-zargen rundunar ‘yan sanda na cewa magoya bayan Ibrahim Zakzaky sun harbi ‘yan sandan uku. Wannan wata motar ‘yan sanda ce da masu zanga-zangar suka lalata.
Wani wurin duba motoci da masu zanga-zangar suka lalata sannan suka yi rubutun nuna kin jinin tsare shugaban kungiyarsu Ibrahim Zakzaky.