Kalaman Buhari a kan satar kuri’a ta tayar da kura

Shugaba Muhammadu Buhari

Hakkin mallakar hoto
TWITTER/@BASHIRAHMAAD

‘Yan Najeriya na ci gaba da yin muhawara a game da gargadin da shugaban kasar ya yi cewa duk dan siyasar da ya yi yunkurin satar kuri`a a manya zabukan kasar da ke tafe, to ya yi ne a bakin ransa.

Tuni dai babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta soki wadannan kalaman na shugaban kasar a cikin wata sanarwa da ta fitar.

PDP ta ce tana fatan wannan kiran da shugaban ya yi ba wata makarkashiya ba ce ta bai wa wadanda ta kira sojojin bogi da jam’iyyar ta tattara damar harbe ‘yan Najeriya su kuma kwace akwatunan zabe su yi aringizon kuri’u a ranar zaben.

Abdullahi Umar, wani dan Najeriya ne da ke cewa shi a ra’ayinsa tun da Najeriya kasa ce da dokoki ya kamata a bi doka wajen yanke hukunci a kan kowanne irin laifi.

Abdullahi ya ce yin karan tsaye da tsallake abin da kundin tsarin mulki ya tanadar ka iya jefa rayukan ‘yan kasa cikin hadari kasancewa ba a taru an zama daya ba.

Shi ma ana sa ra’ayin Ahmed Usman, ya ce wannan ra’ayi ne irin na shugaban kasa domin akwai hanyoyi da dama da za a iya bi wajen dakile satar kuri’a ba sai ta hanyar harbi ko barazana ga rai ba.

Sai dai kwamitin kamfe na Shugaba Buhari a ta bakin Honourable Faruk Adamu Aliyu, ya ce an yi wa kalaman shugaban mummunar fahimta.

A ranar 16 ga watan Fabrairun 2019 ne hukumar zaben Najeriya ta dage babban zabenta sa’o’i kalilan kafin fara zaben.

Hakan ya jawo ce-ce-ku-ce daga wasu daga cikin ‘yan kasar da ma jam’iyyun siyasa bisa dage wannan zabe sa’oi kadan kafin a fara gudanar da shi.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...