Wasu ‘yan bindiga da ba a tantance ba sun kashe akalla mutane 66 a karamar hukumar Kajuru da ke jihar Kaduna a ranar Juma’a.
Gwamnatin Kaduna da ta tabbatar da labarin ta ce harin ya fi shafar mata da yara kanana, inda aka kashe yara 22 da mata 12.
Harin kuma ya shafi rugagen Fulani da dama da ke cikin karamar hukumar Kajuru da suka hada da Ruga da Bahago da Ruga Daku da Ruga Ori da Ruga Haruna da Rugar Yukka Abubakar da Ruga Duni Kadiri da Ruga Shewuka da Ruga Shuaibu Yau.
Gwamnatin Kaduna ta yi Allah wadai da harin, inda gwamnan jihar Nasir el-Rufa’i a cikin wata sanarwa da ya wallafa a Twitter ya bayyana cewa ya tura jami’an tsaro a yankin.
Kuma gwamnan ya ce tuni aka kama wasu daga cikin maharan.
An kai harin ne a jajibirin zabe, inda ‘yan Najeriya ke shirin kada kuri’ar zaben shugaban kasa.
Karin bayani na tafe…