Jirgin yaƙin sojin saman Najeriya ‘ya faɗi’ a Borno

jirgin yakin najeriya

Asalin hoton, Nigerian Airforce

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce watakila jirgin nan nata da ya yi ɓatan dabo ranar Laraba faɗuwa ya yi.

Wata sanarwa da Daraktan yaɗa labarai na rundunar Air Commodore Edward Gabkwet, ya fitar ranar Juma’a ta ce bayanan sirrin da suka tattara sun nuna cewa jirgin samfurin Alpha Jet aircraft (NAF475) wanda na’urar da ke hango zirga-zirgar jirage da tuntuɓarsu wato radar ta kasa ganinsa, yana ɗauke da mutum biyu.

“Ba a san abin da ya haddasa hatsarin ba da kuma inda matuka jirgi biyu suke. Matuka jirgin su ne Flight Lieutenant John Abolarinwa da Flight Lieutenant Ebiakpo Chapele,” in ji sanarwar.

Air Commodore Gabkwet ya kara da cewa jiragen sojin sama masu bincike da dakarun sojan sama na musamman da kuma dakarun sojin kasa suna ci gaba da neman jirgin.

“A halin yanzu, rundunar sojin sama ba za ta iya tabbatar da ainihin abin da ya faru ba game da hatsarin. Sai dai tana fatan nan ba da jimawa ba za a gano matua jirgin,” in ji shi.

Tun da farko rundunar sojin saman ta Najeriya ta ce na’urar da ke hango zirga-zirgar jirage da tuntuɓarsu wato radar ta kasa ganin inda wani jirgin rundunar sojin saman Najeriya ya shiga.

Jirgin yaƙin yana kan wani aiki ne na taimakon dakarun rundunar sojin ƙasa a jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar.

Air Commodore Gabkwet, ya ce “an daina jin ɗuriyar jirgin ne tun ƙarfe biyar na yammacin Laraba 31 ga watan Maris.”

“Har yanzu babu wasu bayanai kan inda jirgin ya shiga ko dalilin ɓacewarsa, amma za mu sanar da al’umma da zarar mun gano wani abu,” a cewarsa.

Aikin da jirgin ke yi wani ɓangare ne na ci gaba da yaƙi da ƴan ƙungiyar Boko Haram da ake yi.

Rundunar ba ta kuma yi bayani kan ko mutum nawa ne ke cikin jirgin ba.

Jaridar Punch ta ruwaito wani tsohon kwamanda a rundunar sojin saman ƙasar na cewa “idan har aka yi minti 30 ba a ji ɗuriyar jirgin yaƙi ba to za a ayyana cewa wannan jirgi ya ɓata ne.”

A watan Fabrairun da ya gabata ma wani jirgin yaƙin rundunar sojin saman ƙasar ya yi hatsari a Abuj kan hanyarsa ta zuwa Minna, inda dukkan jami’ai bakwai da ke cikinsa suka mutu.

More News

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...

Musulmi a Zaria sun yi taron addu’o’i saboda mummunan halin matsi da Najeriya ke ciki

Musulmi a garin Zaria na jihar Kaduna, sun gudanar da addu'a ta musamman domin neman taimakon Allah kan halin da 'yan Najeriya ke ciki...