Jinsin jakai na barazanar karewa a duniya | BBC Hausa

Jakuna uku

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Fasa-kwauri da cinikin fatun jakai, abu ne da ke ci gaba da jan hankalan masu ruwa da tsaki da mahukunta a fadin duniya.

Sun ce yanka dabbobin ba ya rasa nasaba da gagarumin neman da ake masu a kasar China wajen hada magungunan gargajiya.

A makon jiya ne majalisar dokokin Nijeriya ta yi zaman jin ra’ayoyin jama’a kan wani kudurin doka na Honarabul Garba Datti Muhammad da ke neman haramta yanka da fataucin jakai zuwa ketare.

Cikin mahalarta zaman, har da jami’an wata gidauniya ceto jakai mai fafutuka don inganta rayuwar jakan da alfadarai da ma mutane ta Burtaniya.

Simon Pope, babban jami’i a gidauniyar Donkey Sanctuary ta kasar Birtaniya ya ce abin bakin ciki ne idan aka yi la’akari da amfanin jaki a rayuwar dan adam a matsayin wani abun sufuri kamar mota.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Mista Pope ya kuma ce mafi yawan fatun da ake safara suna fitowa ne daga Afirka.

Ya ce “Najeriya musamman na jan hankalin masu sayen fatar jakai saboda yawansu a nan.”

Ya kuma ce a kalla akwai jakai miliyan daya da dubu dari uku a kasar.

“Sai dai wani dan kasuwa ya bayyana cewa ana yanka a kalla jakai dubu biyu da dari biyar a kasuwarsu kullum”, in ji Mista Pope.

Hakan kuma ya nuna ana kashe jakai kusan dubu dari shida duk shekara.

Ya ce duk da cewa jakan Najeriya na da yawa, amma da wannan adadin da ake yankawa za a wayi gari babu jaki ko daya a kasar.

Mista Pope ya ce rayuwar jakuna na da muhimmanci matuka saboda irin gudumawar da suke bayarwa wajen taya aikace-aikace musamman ma a Najeriya.

Da yawa daga cikin mutanen karkara a Najeriyar dai sun ta’allaka kan jaki a matsayin abin hawa zuwa kasuwa da zuwa gonaki har da kai iyalai asibiti a lokutan haihuwa.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...