Jami’ar Bayero ta samu lasisin bude gidan talabijin | BBC Hausa

Jami'ar Bayero ta yi fice wurin karantar da aikin jarida a Najeriya

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Hukumar kula da kafafen yada labaru ta Najeriya, NBC, ta bai wa jami’ar Bayero da ke Kano lasisin da zai ba ta damar kafa gidan talabijin.

Wannan lasisi da jami’ar ta samu zai ba ta damar kafa gidan talabijin na kanta ta yadda za ta rinka koyar da dalibai aikin yada labaru na talabijin, a cewar shugaban hukumar ta NBC Ishaq Kawu.

Shugaban na NBC dai ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin jami’ar ta Bayero da ke Kano.

Yanzu haka dai jami’ar tana da gidan rediyo wanda ke yada labaru daga harabarta.

Shugaban bangaren karatun gaba da digiri na jami’ar Farfesa Umar Pate ya shaida wa BBC cewa sun samu tallafin kudaden gina dakin gabatar da shirye-shirye na gidan talabijin din daga wasu kungiyoyi.

Farfesan, wanda shi ne ya jagoranci sake gina gidan rediyon da samar masa da kayan aiki na zamani, ya ce nan gaba za a fara aiki domin gina gidan talabijin din.

Shugaban jami’ar Farfesa Muhammad Yahuza Bello ya ce wannan lasisi zai bunkasa harkar yada labaru a Najeriya.

Ya kara da cewa za a yi amfani da lasisin wajen horas da dalibai aikin jarida na binciken kwakwaf.

Jami’ar Bayero na daga cikin jami’o’in da suka yi fice a fannin koyar da aikin jarida a kasar.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...