Jami’an tsaro sun sake kama wani kusa a jam’iyar PDP a Kaduna

Jami’an tsaro sun kama Yaro Makama, jigo a jam’iyar PDP ta jihar Kaduna.

Kamun nasa na zuwa ne kasa da sa’o’i 24 bayan da aka kama, Ben Bako daraktan yada labaran yakin neman zaben jam’iyar PDP a Kaduna aka kuma tasa keyarsa a jirgin sama ya zuwa birnin tarayya Abuja.

An kama Bako ne saboda yin kalaman tayar da hankali cikin wani fefan bidiyo da aka dauka a lokacin da jam’iyyar ta ke gangamin yakin neman zabe a garin Kafanchan dake karamar hukumar Jama’a a makon da ya gabata.

Da yake magana kan lamarin mataimakin daraktan yakin neman zaben jam’iyar, Danjuma Sarki ya bayyana cewa wannan wani shiri ne na murkushe ƴaƴan jam’iyar gabanin zabe mai zuwa..

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...