Itacen girki na karanci a Maiduguri

Mayakan Boko Haram sun sha kai harin kunar bakin wake kan al'umma a Maiduguri

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

A garin Maiduguri babban birnin jihar Borno, da ke arewa-maso-gabashin Najeriya jama’a na kokawa game da karancin itacen girki da kuma gawayi.

To ko me ya jawo hakan?

Wani mutum da ya dogara da sana’ar shigo da itacen girki da gawayi daga wasu jahohin na Najeriya ya ce jami’an tsaro kan hana motoci masu dauke da itacen ko kuma gawayi shiga birnin na Maiduguri.

A cewarsa ‘Amma na ji an ce an dauki wannan mataki ne saboda tsaro.’

Ya kuma kara da cewa a yanzu itacen girki da ake sayarwa Naira 250 ya kara farashi zuwa Naira 300.

Jihar Borno dai ita ce a tsakiyar matsalar tsaro na rikicin Boko Haram, wanda aka kwashe sama da shekara 10 ana fama da shi.

A kwanakin baya, mayakan Boko Haram sun rinka amfani da daidaikun mutane ko yara mata wajen kai harin kunar-bakin-wake kan al’umma a birnin Maiduguri.

A baya-bayan nan kuma mayakan sun tsananta kai hare-hare kan sojojin Najeriya, gabanin babban zaben kasar na shekarar 2019.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...