Itacen girki na karanci a Maiduguri

Mayakan Boko Haram sun sha kai harin kunar bakin wake kan al'umma a Maiduguri

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

A garin Maiduguri babban birnin jihar Borno, da ke arewa-maso-gabashin Najeriya jama’a na kokawa game da karancin itacen girki da kuma gawayi.

To ko me ya jawo hakan?

Wani mutum da ya dogara da sana’ar shigo da itacen girki da gawayi daga wasu jahohin na Najeriya ya ce jami’an tsaro kan hana motoci masu dauke da itacen ko kuma gawayi shiga birnin na Maiduguri.

A cewarsa ‘Amma na ji an ce an dauki wannan mataki ne saboda tsaro.’

Ya kuma kara da cewa a yanzu itacen girki da ake sayarwa Naira 250 ya kara farashi zuwa Naira 300.

Jihar Borno dai ita ce a tsakiyar matsalar tsaro na rikicin Boko Haram, wanda aka kwashe sama da shekara 10 ana fama da shi.

A kwanakin baya, mayakan Boko Haram sun rinka amfani da daidaikun mutane ko yara mata wajen kai harin kunar-bakin-wake kan al’umma a birnin Maiduguri.

A baya-bayan nan kuma mayakan sun tsananta kai hare-hare kan sojojin Najeriya, gabanin babban zaben kasar na shekarar 2019.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...