INEC ta amince jam’iyu su cigaba da yakin neman zabe

Hukumar Zabe ta kasa INEC, ta ce a yanzu jam’iyun siyasa za su iya cigaba da yakin neman zabe gabanin sabuwar ranar da aka saka ta zaben shugaban kasa.

Hukumar ta bayar da wannan umarnin ne bayan wani taro da tayi ranar Litinin a Abuja.

Tun da farko shugaban hukumar, Mahmoud Yakubu ya ce ba za a cigaba da yakin neman zabe ba duk da dage ranar zaben shugaban kasa da na yan majalisun tarayya da aka yi.

Amma kuma bayan zaman ganawar da shugabannin hukumar suka yi hukumar ta ce yan takarar shugaban kasa da kuma jam’iyun siyasa za su cigaba da yakin neman zabe har ya zuwa daren ranar Alhamis.

Ko da a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyar APC da ta gudanar a yau jam’iyar taci alwashin cigaba da yakin neman zabe duk da cewa hakan yaci karo da umarnin INEC.

Dokar zabe ta bayyana za a dakatar da yakin neman zabe ne sa’o’i 24 gabanin a fara kada kuri’a.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...