INEC ta amince jam’iyu su cigaba da yakin neman zabe

Hukumar Zabe ta kasa INEC, ta ce a yanzu jam’iyun siyasa za su iya cigaba da yakin neman zabe gabanin sabuwar ranar da aka saka ta zaben shugaban kasa.

Hukumar ta bayar da wannan umarnin ne bayan wani taro da tayi ranar Litinin a Abuja.

Tun da farko shugaban hukumar, Mahmoud Yakubu ya ce ba za a cigaba da yakin neman zabe ba duk da dage ranar zaben shugaban kasa da na yan majalisun tarayya da aka yi.

Amma kuma bayan zaman ganawar da shugabannin hukumar suka yi hukumar ta ce yan takarar shugaban kasa da kuma jam’iyun siyasa za su cigaba da yakin neman zabe har ya zuwa daren ranar Alhamis.

Ko da a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyar APC da ta gudanar a yau jam’iyar taci alwashin cigaba da yakin neman zabe duk da cewa hakan yaci karo da umarnin INEC.

Dokar zabe ta bayyana za a dakatar da yakin neman zabe ne sa’o’i 24 gabanin a fara kada kuri’a.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...