{"id":69971,"date":"2018-12-15T07:00:22","date_gmt":"2018-12-15T06:00:22","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=69971"},"modified":"2018-12-15T07:00:39","modified_gmt":"2018-12-15T06:00:39","slug":"rundunar-sojin-najeriya-tayi-amai-ta-lashe-a-kan-unicef","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=69971","title":{"rendered":"Rundunar Sojin Najeriya tayi amai ta lashe a kan UNICEF"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Hukumar UNICEF na tallafawa 'yan gudun hijirar da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2018\/12\/Rundunar-Sojin-Najeriya-tayi-amai-ta-lashe-a-kan-UNICEF.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><br \/>\n<span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nHukumar UNICEF na tallafawa &#8216;yan gudun hijirar da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu<\/span><figcaption class=\"media-caption\"><\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Rundunar sojin Najeriya ta soke matakin dakatar da ayyukan asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF a arewa maso gabashin kasar kamar yadda ta sanar da farko.<\/p>\n<p>Rundunar dai ta zargi UNICEF da zagon-kasa ga kokarin da sojoji ke yi na yaki da Boko Haram ta hanyar horarwa da kuma tura &#8216;yan leken asirin Boko Haram.<\/p>\n<p>Sai dai a yanzu kusan ana iya cewa rundunar tayi amai ta lashe, bayan wani taron gaggawa da tace ta gudanar da wakilan UNICEF.<\/p>\n<p>Wata sanawar dauke da sa hannu mataimakin daraktan hulda da jama&#8217;a na rundunar, Kanar Onyema Nwachukwu, ta ce a lokacin tattaunawar, sun shaidawa hukumar ta agaji kar ta kuskura ta yi kafar ungulu ga ayyukan sojin a arewa maso gabashin kasar.<br \/>\nHaka nan kuma an umarci wakilan UNICEF da su ringa sanar da mahukunta a duk lokacin da za su bai wa sabbin ma&#8217;aikatansu horo.<\/p>\n<p>Da fari dai, rundunar ta fitar da sanarwar da ke zargin UNICEF da yin zagon-kasa a yakin da ake da Boko Haram ta hanyar yada labaran karya ko marasa sahihanci.<\/p>\n<p>Wannan ba shi ne karon farko da rundunar ke kwan-gaba kwan-baya a kan matakin da suke dauka kan UNICEF ba.<\/p>\n<p>Ko a wata Afrilu, ta bayyana wasu ma&#8217;aikatan hukumar uku da ta ce ba a bukatar aikinsu a kasar, sakamakon zargin cin zarafi ta hanyar lalata da aka kwarmata a kan sojojin Najeriya.<\/p>\n<p>Sai dai daga baya rundunar ta sauya shawara tare da janye kalamanta.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hukumar UNICEF na tallafawa &#8216;yan gudun hijirar da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu Rundunar sojin Najeriya ta soke matakin dakatar da ayyukan asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF a arewa maso gabashin kasar kamar yadda ta sanar da farko. Rundunar dai ta zargi UNICEF da zagon-kasa ga kokarin da sojoji [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":69972,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[],"class_list":["post-69971","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/69971","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=69971"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/69971\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/69972"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=69971"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=69971"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=69971"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}