{"id":69882,"date":"2018-12-15T07:03:19","date_gmt":"2018-12-15T06:03:19","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=69882"},"modified":"2018-12-15T07:03:24","modified_gmt":"2018-12-15T06:03:24","slug":"mohamed-salah-ne-zakaran-kwallon-kafar-afirka-na-bbc","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=69882","title":{"rendered":"Mohamed Salah ne zakaran kwallon kafar Afirka na BBC"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape has-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Mohamed Salah\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2018\/12\/Mohamed-Salah-ne-zakaran-kwallon-kafar-Afirka-na-BBC.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><figcaption class=\"media-caption\"><span class=\"media-caption__text\"><br \/>\nKaro na biyu ke nan Mohamed Salah yana lashe gasar a jere<\/span><br \/>\n<\/figcaption><\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">An zabi dan wasan kwallon kafa na Egypt kuma na kungiyar Liverpool Mohamed Salah a matsayin dan wasan da ya fi kowanne taka leda sau biyu a jere.<\/p>\n<p>Dan wasan mai shekara 26 ya doke Medhi Benatia da Kalidou Koulibaly da Sadio Mane da Thomas Partey, ya lashe lambar.<\/p>\n<p>&#8220;Abun farin ciki ne,&#8221; Salah ya shaida wa BBC.<\/p>\n<p>&#8220;Zan so a shekara mai zuwa ma in sake yin nasara. Ina farin ciki da yin wannan nasara.&#8221;<\/p>\n<p>Dan wasan da ya lashe lambar yabo ta Gasar zakarun Turai na bana ya zira wa Liverpool kwallo 44 a raga a wasanni 52 a kakar da ta wuce kuma ya taimaka wa kungiyar kai wa zagayen karshe a kasar Zakarun Turai.<\/p>\n<p>&#8220;Ko wane lokaci, ina ji kamar na ci kwallo, ina taimakon kungiyar kulob din ya samu maki a gasar, wannan a koyaushe abu ne mai faranta rai.&#8221;<\/p>\n<p>Ya ci wa Masar kwallo sau biyu a gasar cin kofin kofin duniya ta bana.<\/p>\n<p>BBC ta samu kuri&#8217;u sama da 650,000 a bana &#8211; wanda wannan shi ne adadi mafi yawa da aka taba samu.<\/p>\n<p>Salah ya zama dan wasa na farko da ya lashe kyautar sau biyu tun bayan JayJ Okocha.<\/p>\n<p>Tsohon dan wansan na Chelsea ya sanya hannu da kulob din Liverpool bayan ya baro Roma a kakar 2017. Ya ci kwallo 15 sannan ya taimakawa Roma ta ci kwallo 11, wacce ta gama gasar Seria A a mataki na biyu.<\/p>\n<p>Ya fara wasansa a Liverpool da kafar dama, inda ya zura kwallo 19 a raga a wasanni 24.<\/p>\n<p>Ya share nasarorin da aka yi a baya na kwallaye 31 a wasa 38 a kakar gasar firimiya, wadanda Luis Suarez suka ci a 2013-14, da Cristiano Ronaldo a 2007-08, da kuma Alan Shera a 1995-96.<\/p>\n<p>Mohamed Barakat (2005) da Mohamed Aboutrika (2008) su ne sauran &#8216;yan Masar din da suka lashe gasar.<\/p>\n<hr class=\"story-body__line\">\n<h2 class=\"story-body__crosshead\">Wadanda suka lashe gasar a baya<\/h2>\n<p>&#8216;Yan wasan da suka lashe gasar a baya<\/p>\n<p>2017: Mohamed Salah (Liverpool da Egypt)<\/p>\n<p>2016: Riyad Mahrez (Leicester City da Algeria)<\/p>\n<p>2015: Yaya Toure (Manchester City da Ivory Coast)<\/p>\n<p>2014: Yacine Brahimi (Porto da Algeria)<\/p>\n<p>2013: Yaya Toure (Manchester City da Ivory Coast)<\/p>\n<p>2012: Chris Katongo (Henan Construction da Zambia)<\/p>\n<p>2011: Andre Ayew (Marseille da Ghana)<\/p>\n<p>2010: Asamoah Gyan (Sunderland da Ghana)<\/p>\n<p>2009: Didier Drogba (Chelsea da Ivory Coast)<\/p>\n<p>2008: Mohamed Aboutrika (Al Ahly da Egypt)<\/p>\n<p>2007: Emmanuel Adebayor (Arsenal da Togo)<\/p>\n<p>2006: Michael Essien (Chelsea da Ghana)<\/p>\n<p>2005: Mohamed Barakat (Al Ahly da Egypt)<\/p>\n<p>2004: Jay-Jay Okocha (Bolton da Nigeria)<\/p>\n<p>2003: Jay-Jay Okocha (Bolton da Nigeria)<\/p>\n<p>2002: El Hadji Diouf (Liverpool da Senegal)<\/p>\n<p>2001: Sammy Kuffour (Bayern Munich da Ghana)<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Karo na biyu ke nan Mohamed Salah yana lashe gasar a jere An zabi dan wasan kwallon kafa na Egypt kuma na kungiyar Liverpool Mohamed Salah a matsayin dan wasan da ya fi kowanne taka leda sau biyu a jere. Dan wasan mai shekara 26 ya doke Medhi Benatia da Kalidou Koulibaly da Sadio Mane [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":69883,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[],"class_list":["post-69882","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/69882","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=69882"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/69882\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/69883"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=69882"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=69882"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=69882"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}