{"id":68998,"date":"2018-12-12T06:09:12","date_gmt":"2018-12-12T05:09:12","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=68998"},"modified":"2018-12-12T06:09:17","modified_gmt":"2018-12-12T05:09:17","slug":"dalilin-da-ya-sa-atiku-ya-kauracewa-taron-zaman-lafiya","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=68998","title":{"rendered":"Dalilin da ya sa Atiku ya kauracewa taron zaman lafiya"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Atiku Abubakar dan takarar jam'iyyar PDP\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2018\/12\/Dalilin-da-ya-sa-Atiku-ya-kauracewa-taron-zaman-lafiya.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<p>Dan takarar shugaban kasa na Jam&#8217;iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana dalilin da ya sa ya kauracewa taron tabbatar da zaman lafiya a zaben 2019.<\/figure>\n<p>Tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce bai san da taron ba domin ba a gayyace shi ba, kamar yadda kakakinsa Paul Ibe ya fitar da sanarwa a Twitter.<\/p>\n<p>&#8220;Babu wani goron gayyata da Atiku ya samu domin halartar taron kulla yarjejeniyar ta zaman lafiya,&#8221; in ji shi.<\/p>\n<p>Sai dai kuma wanda ya jagoranci kulla yarjejeniyar, tsohon shugaban kasa Abdussalam Abubakar ya shaida wa BBC cewa sai da suka zauna tare da dukkanin jam&#8217;iyyun siyasar Najeriya aka cimma matsaya.<\/p>\n<p>An tambaye shi game da ikirarin bangaren Atiku kan rashin gayyatar shi, sai tsohon shugaban ya ce &#8220;Me zai sa ba za mu gayyace shi ba, kuma me zai sa ba za mu gayyaci kowa ba?&#8221;<\/p>\n<p>Muna zance ne yadda za a gaya wa mutane a yi siyasa ba da gaba ba, to me zai sa na dauki mutum guda na ce ba zan gayyace shi ba,&#8221; in ji Janar Abdussalam.<\/p>\n<ul class=\"story-body__unordered-list\"><\/ul>\n<p>Shugaba Muhammadu Buhari na jam&#8217;iyyar APC da wasu &#8216;yan takarar da dama sun halarci taron kuma sun sa hannu a &#8216;yarjejeniyar.<\/p>\n<p>An sa hannun ne a kan idon malaman addinai da sarakunan gargajiya da kuma jakadu na kasashen Turai.<\/p>\n<h2 class=\"story-body__crosshead\">Abin da yarjejeniyar ta kunsa<\/h2>\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width\"> <\/figure>\n<p>Yarjejeniyar da tsohon shugaban mulkin soji na Najeriya ke jagoranta ta bukaci &#8216;yan takara da jam&#8217;iyyunsu su tabbatar da zaman lafiya a lokacin zabe da kuma bayan zaben.<\/p>\n<p>Yarjejeniyar kuma ta bukaci a kaucewa duk wasu kalamai na batanci ga addinin wani ko kabila.<\/p>\n<p>Sannan ta shafi kaucewa duk wani abu da zai kai ga haifar da tashin hankali a lokacin zabe.<\/p>\n<p>Irin wannan yarjejeniyar ce aka kulla kafin zaben 2015 inda ake ganin ta taka rawa sosai ga sauyin shugabanci daga jam&#8217;iyya mai mulki zuwa ta hamayya ba tare da an samu wani tashin hankali ba.<\/p>\n<p>A lokacin zaben 2015, tun kafin a kammala kidaya kuri&#8217;un zaben shugaban kasa, shugaba mai ci Goodluck Jonathan ya kira abokin takararsa Muhammadu Buhari ya amsa shan kaye.<\/p>\n<p>Yanzu kuma ana ganin kauracewa taron kulla yarjejeniyar da dan takarar adawa Alhaji Atiku Abubakar ya yi babban kalubale ne ga samun nasarar yarjejeniyar a zaben na badi.<\/p>\n<p>Ko da yake tsohon shugaban ya ce baya jin rashin zuwan dan takarar na PDP ma hamayya zai shafi ingancin yarjejeniyar da aka kulla.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Dan takarar shugaban kasa na Jam&#8217;iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana dalilin da ya sa ya kauracewa taron tabbatar da zaman lafiya a zaben 2019. Tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce bai san da taron ba domin ba a gayyace shi ba, kamar yadda kakakinsa Paul Ibe ya fitar da sanarwa a Twitter. &#8220;Babu [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":68999,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[],"class_list":["post-68998","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/68998","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=68998"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/68998\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/68999"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=68998"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=68998"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=68998"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}