{"id":66816,"date":"2018-12-04T11:53:12","date_gmt":"2018-12-04T10:53:12","guid":{"rendered":"https:\/\/arewa.ng\/?p=66816"},"modified":"2018-12-04T11:53:25","modified_gmt":"2018-12-04T10:53:25","slug":"efcc-za-ta-gurfanar-da-diezani-a-gaban-kotu","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/arewa.ng\/?p=66816","title":{"rendered":"EFCC za ta gurfanar da Diezani a gaban kotu"},"content":{"rendered":"<div property=\"articleBody\">\n<figure class=\"media-landscape no-caption full-width lead\"><img fetchpriority=\"high\" decoding=\"async\" class=\"js-image-replace\" alt=\"Mrs Diezani\" src=\"http:\/\/arewa.ng\/wp-content\/uploads\/2018\/12\/EFCC-za-ta-gurfanar-da-Diezani-a-gaban-kotu.jpg\" width=\"976\" height=\"549\"><\/p>\n<\/figure>\n<p class=\"story-body__introduction\">Hukumar EFCC da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya ta&#8217;annati ta ce za ta gurfanar da tsohuwar ministar man fetur ta kasar, Mrs Diezani Alison-Madueke a gaban kuliya kan zargin cin hanci da rashawa.<\/p>\n<p>A sanarwar da mai magana da yawun hukumar Mr Tony Orilade ya aike wa manema labarai ranar Litinin da yamma, ya ce a watan Fabrairun 2019 ne za a gurfanar da Mrs Alison-Madueke da kuma tsohon shugaban kamfanin tatar mai na Atlantic Energy Drilling Company, Jide Omokore kan zargin aikata laifuka biyar.<\/p>\n<p>A cewar EFCC, ana zargin mutanen biyu da karbar hanci da kyautuka a wurare biyu &#8211; dukka a birnin Lagos, lamarin da ya saba wa dokar hana karbar hanci da rashawa.<\/p>\n<p>EFCC ta kara da cewa ta samu izinin gurfanar da mutanen biyu a gaban kuliya daga mai sharia Valentine Ashi ta babbar kotun birnin Abuja ranar uku ga watan Disamba.<\/p>\n<p>Hukumar ta nemi izini daga kotun domin ta samu damar taso keyar Mrs Madueke daga Burtaiya inda take zaune tun shekarar 2015.<\/p>\n<p>EFCC ta shaida wa kotun cewa ta dade da aike wa tsohuwar ministar takardar gayyata zuwa Najeriya domin ta kare kanta daga zarge-zargen cin hancin da ake yi mata amma ta ki amsa gayyatar.<\/p>\n<p>Da ma dai hukumar ta dade tana so a ba ta umarnin gurfanar da tsohuwar ministar man a kotun da ke Najeriya.<\/p>\n<p>Tsohuwar ministar na cikin manyan jami&#8217;an tsohuwar gwamnatin Shugaba Goodluck Jonathan da ake zargi da cin hanci, ko da yake ta sha musanta zargin.<\/p>\n<p>Ta fice daga Najeriya zuwa Burtaniya jim kadan bayan Muhammadu Buhari ya kayar da Mr Jonathan a zaben 2015.<\/p>\n<p>A watan Aprilun 2016, EFCC ta kwace gwala-gwalan da darajarsu ta kai N593m daga hannun tsohuwar ministar.<\/p>\n<p>Kazalika, a watan Agustan 2017, wata babbar kotun da ke Lagos ta mallaka wa gwamnatin Najeriya kaddarorin Mrs Diezani Alison-Madueke, da suka kai $40, wato kimanin naira biliyan 14.<\/p><\/div>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"<p>Hukumar EFCC da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya ta&#8217;annati ta ce za ta gurfanar da tsohuwar ministar man fetur ta kasar, Mrs Diezani Alison-Madueke a gaban kuliya kan zargin cin hanci da rashawa. A sanarwar da mai magana da yawun hukumar Mr Tony Orilade ya aike wa manema labarai ranar Litinin [&hellip;]<\/p>\n","protected":false},"author":1,"featured_media":66817,"comment_status":"open","ping_status":"closed","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","jetpack_publicize_message":"","jetpack_publicize_feature_enabled":true,"jetpack_social_post_already_shared":true,"jetpack_social_options":{"image_generator_settings":{"template":"highway","default_image_id":0,"font":"","enabled":false},"version":2}},"categories":[2681],"tags":[],"class_list":["post-66816","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","hentry","category-hausa"],"jetpack_publicize_connections":[],"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/66816","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/users\/1"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcomments&post=66816"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/posts\/66816\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=\/wp\/v2\/media\/66817"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fmedia&parent=66816"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Fcategories&post=66816"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/arewa.ng\/index.php?rest_route=%2Fwp%2Fv2%2Ftags&post=66816"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}